Koma ka ga abin da ke ciki

Koma ga abubuwan da ke ciki

Gabatarwar Sashe na 4

Gabatarwar Sashe na 4

Wannan sashen ya yi magana game da Yusufu da Ayuba da Musa da kuma Isra’ilawa. Dukansu sun jimre da jarraba daga Shaiɗan. An yi wa wasu daga cikinsu rashin adalci, an tura wasu kurkuku, wasu an mai da su bayi, wasu kuma sun yi rashin ʼyan’uwansu babu zato. Amma Jehobah ya cece su a hanyoyi da yawa. Idan kana da yara, ka taimaka musu su fahimci yadda waɗannan bayin Allah suka ci gaba da bauta wa Jehobah duk da wahalar da suka sha.

Jehobah ya yi amfani da Annoba Goma don ya nuna cewa ya fi dukan allolin Masar ƙarfi. Ka nuna yadda Jehobah ya kāre bayinsa a dā da kuma yadda yake yin hakan a yau.

A WANNAN SASHEN

DARASI NA 14

Wani Bawa da Ya Yi Biyayya ga Allah

Yusufu ya yi abin da ya dace amma duk da haka, ya sha wahala sosai. Me ya sa?

DARASI NA 15

Jehobah Bai Manta da Yusufu Ba

Duk da cewa Yusufu ya yi nesa da danginsa, Allah ya ci gaba da kasancewa tare da shi.

DARASI NA 16

Wane Irin Mutum Ne Ayuba?

Ya yi wa Jehobah biyayya duk da cewa hakan bai yi masa sauki ba.

DARASI NA 17

Musa Ya Bauta wa Jehobah

Sa’ad da Musa yake jariri, mahaifiyarsa ta cece shi don basirar da ta yi.

DARASI NA 18

Bishiya Mai Cin Wuta

Me ya sa wutar ba ta cinye bishiyar ba?

DARASI NA 19

Annoba ta Daya Zuwa Uku

Fir’auna janyo annoba wa mutanensa saboda da fahariyarsa bai kyale shi ya yi abin da ya kamata ya yi ba.

DARASI NA 20

Annoba ta Hudu Zuwa Tara

Mene ne bambancin da ke tsakanin annobar nan da sauran guda ukun?

DARASI NA 21

Annoba ta Goma

Wannan annobar ta yi muni sosai, har ta sa Fir’auna da kansa ya yi biyayya.

DARASI NA 22

Abu Mai Ban Mamaki a Jar Teku

Annoba guda goma ba su kashe Fir’auna ba, amma wannan mu’ujizar da Allah ya yi ya kashe shi.