Koma ka ga abin da ke ciki

Koma ga abubuwan da ke ciki

Gabatarwar Sashe na 10

Gabatarwar Sashe na 10

Jehobah shi ne Sarkin duniya gabaki ɗaya. Shi ne yake iko kuma zai ci gaba da kasancewa da iko. Alal misali, ya ceci Irmiya daga wata rijiyar da aka jefa shi ciki don ya mutu. Ya ceci Shadrach da Meshach da kuma Abednego daga wuta mai zafi. Ya kuma ceci Daniyel daga hannun zakuna. Jehobah ya kāre Esther don ta iya ceton mutanenta. Ba zai bar mutane su ci gaba da yin mugunta har abada ba. Annabcin da aka yi game da babban gunki da kuma bishiya sun nuna cewa Mulkin Jehobah zai mulki duniyar nan kuma zai cire mugunta gabaki ɗaya.

A WANNAN SASHEN

DARASI NA 57

Jehobah Ya Aiki Irmiya Ya Yi Wa’azi

Abin da wannan annabin ya ce ya ba wa dattawan Yahuda haushi sosai.

DARASI NA 58

An Halaka Urushalima

Mutanen Yahuda sun ci gaba da bauta wa allolin karya, don haka Jehobah ya rabu da su.

DARASI NA 59

Matasa Hudu da Suka Yi wa Jehobah Biyayya

Wadannan matasa Yahudawan sun kudurta za su rike amincinsu ga Jehobah ko a Babila.

DARASI NA 60

Gwamnatin da Za ta Yi Sarauta Har Abada

Daniyel ya bayyana ma’anar mafarkin Nebuchadnezzar.

DARASI NA 61

Sun Ki Bauta wa Gunki

Shadrach da Meshach da kuma Abednego su ki bauta wa gunki zinariya da sarkin Babila ya yi.

DARASI NA 62

Mulkin da Ke Kama da Babbar Bishiya

Mafarkin Nebuchadnezzar game da kansa ne.

DARASI NA 63

Rubutu a Jikin Bango

Me ya sa rubutu ya bayyana, kuma mene ne rubutu yake nufi?

DARASI NA 64

An Saka Daniyel a Cikin Ramin Zakuna

Kamar yadda Daniyel ya yi, ka rika yi wa Jehobah addu’a a koyaushe!

DARASI NA 65

Esther Ta Ceci Mutanenta

Ta zama sarauniya duk da cewa ita ba ’yar kasar Fasiya ba ce kuma ba ta da iyaye.

DARASI NA 66

Ezra ya koyar da Dokar Allah

Bayan mutanen sun saurari abin Ezra ya gaya musu, sai suka yi alkawari na musamman wa Allah.

DARASI NA 67

Ganuwar Urushalima

Me ya sa Nehemiya bai ji tsoro ba sa’ad da ya ji cewa makiyansa suna sun su kawo masa hari?