WAƘA TA 24
Ku Zo Tudun Jehobah
(Ishaya 2:2-4)
-
1. Muna gayyatar ku
Ku ɗaga idanunku
Don ku ga yadda tudun Allah
Ke da tsayi.
Mutane na zuwa
Daga ko’ina kuma
Suna taruwa sosai
‘Don bauta wa Allah.’
Jehobah na kula
Da mutanensa masu yawa
Kuma mu riƙa bin
Umurnin Allahnmu Jehobah.
Mutane da yawa
Za su bauta wa Allah.
Za su yi alkawarin
Riƙe amincinsu.
-
2. Yesu ya ce mana
Mu je mu yi wa’azi.
Kowa yana bukatar
Jin bisharar Mulki.
Yesu ne Sarkinmu,
Yana gayyatar kowa.
Waɗanda ke biyayya
Allah zai kāre su.
Muna murna sosai,
Mutanen Allah na yin yawa.
Don ƙwazon da muke,
Muna son yin shela ga kowa.
Mu ɗaga muryarmu,
Mu kira kowa ya zo
Tudun Jehobah Allah,
Don su bauta masa.
(Ka kuma duba Zab. 43:3; 99:9; Isha. 60:22; A. M. 16:5.)