Koma ka ga abin da ke ciki

Koma ga abubuwan da ke ciki

WAƘA TA 27

Allah Zai Bayyana ’Ya’yansa

Allah Zai Bayyana ’Ya’yansa

(Romawa 8:19)

  1. 1. Allah Jehobah Ubanmu

    Zai tara shafaffu.

    Za su kasance da Kristi

    A cikin Mulkinsa.

    (AMSHI)

    ’Ya’yan Jehobah Allahnmu,

    Tare da Ɗan Allah,

    Za su halaka mugaye,

    Su yi sarauta ma.

  2. 2. Shafaffun da suka rage

    Za su koma sama

    Domin su kasance tare

    Da Ubangijinmu.

    (AMSHI)

    ’Ya’yan Jehobah Allahnmu,

    Tare da Ɗan Allah,

    Za su halaka mugaye,

    Su yi sarauta ma.

  3. 3. Ɗan Allah da shafaffun nan

    Za su yaƙi Shaiɗan.

    Sai su zama sarakuna

    A Mulkin Allahnmu.

    (AMSHI)

    ’Ya’yan Jehobah Allahnmu,

    Tare da Ɗan Allah,

    Za su halaka mugaye,

    Su yi sarauta ma.

(Ka kuma duba Dan. 2:​34, 35; 1 Kor. 15:​51, 52; 1 Tas. 4:​15-17.)