WAƘA TA 27
Allah Zai Bayyana ’Ya’yansa
(Romawa 8:19)
-
1. Allah Jehobah Ubanmu
Zai tara shafaffu.
Za su kasance da Kristi
A cikin Mulkinsa.
(AMSHI)
’Ya’yan Jehobah Allahnmu,
Tare da Ɗan Allah,
Za su halaka mugaye,
Su yi sarauta ma.
-
2. Shafaffun da suka rage
Za su koma sama
Domin su kasance tare
Da Ubangijinmu.
(AMSHI)
’Ya’yan Jehobah Allahnmu,
Tare da Ɗan Allah,
Za su halaka mugaye,
Su yi sarauta ma.
-
3. Ɗan Allah da shafaffun nan
Za su yaƙi Shaiɗan.
Sai su zama sarakuna
A Mulkin Allahnmu.
(AMSHI)
’Ya’yan Jehobah Allahnmu,
Tare da Ɗan Allah,
Za su halaka mugaye,
Su yi sarauta ma.
(Ka kuma duba Dan. 2:34, 35; 1 Kor. 15:51, 52; 1 Tas. 4:15-17.)