WAƘA TA 34
Mu Zama Masu Aminci
(Zabura 26)
-
1. Ya Allahna, ka ga amincina.
Ka ga ibadata da bangaskiyata.
Ina roƙo ka gwada ni da kyau,
Domin imanina ya yi ƙarfi sosai.
(AMSHI)
Amma ni kam, na ƙudurta cewa
Zan riƙe aminci dukan rayuwata.
-
2. Ba na tarayya da masu ƙarya.
Ba na son mutanen da ba sa gaskiya.
Ya Allahna, kar ka halaka ni
Tare da mutanen da ba sa ƙaunar ka.
(AMSHI)
Amma ni kam, na ƙudurta cewa
Zan riƙe aminci dukan rayuwata.
-
3. Ina ƙaunar gidanka, Ya Allah.
Ina so in riƙa bauta maka kullum.
Zan zagaya a cikin gidanka
Don a ɗaukaka ka a dukan ƙasashe.
(AMSHI)
Amma ni kam, na ƙudurta cewa
Zan riƙe aminci dukan rayuwata.
(Ka kuma duba Zab. 25:2.)