WAƘA TA 36
Mu Rika Kāre Zuciyarmu
(Misalai 4:23)
-
1. Mu lura da zuciyarmu,
Mu guji zunubi.
Allah na ganin zuciya,
Yana ganin kome.
Zuci tana da yaudara,
Takan sa zunubi.
Ya Allah, ka taimake mu
Don mu yi nufinka.
-
2. Mu riƙa addu’a kullum,
Mu kusaci Allah.
Mu miƙa duk damuwarmu
Ga Allah Jehobah.
Za mu riƙa bin umurnin
Jehobah Allahnmu.
Kuma mu riƙe aminci
Don mu sa shi murna.
-
3. Mu daina tunanin banza,
Mu riƙa nagarta.
Mu riƙa barin Kalmarsa
Ta ratsa zucinmu.
Jehobah Allah na sama
Na son mutanensa.
Za mu riƙa bauta masa
Da dukan zuciya.
(Ka kuma duba Zab. 34:1; Filib. 4:8; 1 Bit. 3:4.)