Koma ka ga abin da ke ciki

Koma ga abubuwan da ke ciki

WAƘA TA 36

Mu Rika Kāre Zuciyarmu

Mu Rika Kāre Zuciyarmu

(Misalai 4:23)

  1. 1. Mu lura da zuciyarmu,

    Mu guji zunubi.

    Allah na ganin zuciya,

    Yana ganin kome.

    Zuci tana da yaudara,

    Takan sa zunubi.

    Ya Allah, ka taimake mu

    Don mu yi nufinka.

  2. 2. Mu riƙa addu’a kullum,

    Mu kusaci Allah.

    Mu miƙa duk damuwarmu

    Ga Allah Jehobah.

    Za mu riƙa bin umurnin

    Jehobah Allahnmu.

    Kuma mu riƙe aminci

    Don mu sa shi murna.

  3. 3. Mu daina tunanin banza,

    Mu riƙa nagarta.

    Mu riƙa barin Kalmarsa

    Ta ratsa zucinmu.

    Jehobah Allah na sama

    Na son mutanensa.

    Za mu riƙa bauta masa

    Da dukan zuciya.

(Ka kuma duba Zab. 34:1; Filib. 4:8; 1 Bit. 3:4.)