WAƘA TA 50
Alkawarin Bauta wa Jehobah
(Matta 22:37)
-
1. Na ba Allah zucina
Don ta so dokokinsa.
Na ba Allah muryata
Don ta rera mai yabo.
-
2. Ya Jehobah Allahna,
Na ba ka rayuwata
Da kuma wadatata,
Don in bi umurninka.
-
3. Allah ka taimaka min
Domin in yi nufinka.
Bari duk ayyukana
Su faranta maka rai.
(Ka kuma duba Zab. 40:8; Yoh. 8:29; 2 Kor. 10:5.)