Koma ka ga abin da ke ciki

Koma ga abubuwan da ke ciki

WAƘA TA 58

Muna Neman Mutane Masu Saukin Kai

Muna Neman Mutane Masu Saukin Kai

(Luka 10:6)

  1. 1. Yesu ya ce mu riƙa wa’azi.

    Cikin rana, cikin sanyi,

    Ya yi wa kowa wa’azi.

    Ya yi hakan don yana ƙaunar su.

    Ya yi shela daga safe

    har zuwa yamma.

    Muna zuwa gida-gida

    Domin mu gaya wa kowa

    Allah ya kusan cire wahaloli.

    (AMSHI)

    Muna zuwa

    Yaɗa bisharar Mulkin Allah.

    Muna neman

    Waɗanda ke son samun ceto.

    Fatanmu ne

    Su ji saƙon.

  2. 2. Muna bisharar Mulkin da ƙwazo.

    Maƙwabtanmu, da danginmu,

    Muna so su san gaskiya.

    Ƙauna ce ta sa muke yin hakan,

    Mu riƙa taimakon su,

    su bauta wa Allah.

    Muna shela a ko’ina

    Kuma muna farin ciki,

    Idan mutane na jin wa’azinmu.

    (AMSHI)

    Muna zuwa

    Yaɗa bisharar Mulkin Allah.

    Muna neman

    Waɗanda ke son samun ceto.

    Fatanmu ne

    Su ji saƙon.

(Ka kuma duba Isha. 52:7; Mat. 28:​19, 20; Luk. 8:1; Rom. 10:10.)