WAƘA TA 58
Muna Neman Mutane Masu Saukin Kai
(Luka 10:6)
-
1. Yesu ya ce mu riƙa wa’azi.
Cikin rana, cikin sanyi,
Ya yi wa kowa wa’azi.
Ya yi hakan don yana ƙaunar su.
Ya yi shela daga safe
har zuwa yamma.
Muna zuwa gida-gida
Domin mu gaya wa kowa
Allah ya kusan cire wahaloli.
(AMSHI)
Muna zuwa
Yaɗa bisharar Mulkin Allah.
Muna neman
Waɗanda ke son samun ceto.
Fatanmu ne
Su ji saƙon.
-
2. Muna bisharar Mulkin da ƙwazo.
Maƙwabtanmu, da danginmu,
Muna so su san gaskiya.
Ƙauna ce ta sa muke yin hakan,
Mu riƙa taimakon su,
su bauta wa Allah.
Muna shela a ko’ina
Kuma muna farin ciki,
Idan mutane na jin wa’azinmu.
(AMSHI)
Muna zuwa
Yaɗa bisharar Mulkin Allah.
Muna neman
Waɗanda ke son samun ceto.
Fatanmu ne
Su ji saƙon.
(Ka kuma duba Isha. 52:7; Mat. 28:19, 20; Luk. 8:1; Rom. 10:10.)