WAƘA TA 65
Mu Rika Samun Ci Gaba!
(Ibraniyawa 6:1)
-
1. Mu duƙufa samun ci gaba kullum!
Mu bar kowa ya ga halayenmu masu kyau.
Mu yi himma a yaɗa bisharar nan,
Allah za ya kāre mu.
Dukanmu muna da aikin yi,
Aikin Yesu Ubangijinmu.
Mu roƙi Jehobah ya taimake mu,
Don mu riƙa nagarta.
-
2. Duk mu ƙoƙarta mu riƙa wa’azi!
Mu sanar da saƙon da zai sa a sami rai,
Kuma zai sa a riƙa yabon Allah,
Su yabe shi da ƙwazo.
Maƙiya za su tsorata mu,
Amma kada mu ji tsoron su.
Mu riƙa shelar Mulkin nan da ƙwazo,
Mu yi hakan koyaushe.
-
3. Duk mu ƙoƙarta mu riƙa biyayya,
Mu riƙa inganta
wa’azinmu koyaushe.
Za mu bi ja-gorancin ruhun Allah
Da duk zuciyarmu fa.
Mu ƙaunaci dukan ɗalibai,
Don su so Kalmar Allah sosai.
Su riƙa samun ci gaba koyaushe,
Haskensu ya haskaka.
(Ka kuma duba Filib. 1:27; 3:16; Ibran. 10:39.)