WAƘA TA 75
’Ga Ni! Ka Aike Ni’
(Ishaya 6:8)
-
1. A yau yawancin mutane
Suna ɓata sunan Allah.
Wasu sun ce Shi mugu ne,
Wasu sun musunci Allah!
Wa zai je ya gaya masu?
Wa zai yabi sunan Allah?
(AMSHI NA 1)
‘Ya Allah, aike ni! Zan je!
Zan yabi sunanka sosai.
Gata mafi girma ce Allah.
Ga ni, aike ni! Zan je!’
-
2. Sun ce Allah na jinkiri
Kuma ba su tsoron Allah.
Suna bauta wa gumaka,
Sun mai da Kaisar Allahnsu.
Wa zai gargaɗi mugaye
Don Armageddon ya kusa?
(AMSHI NA 2)
‘Ya Allah, aike ni! Zan je!
Zan yi shela babu tsoro.
Gata mafi girma ce Allah.
Ga ni, aike ni! Zan je!’
-
3. Masu adalci na kuka
Domin mugunta ta ƙaru.
Suna ta neman gaskiya
Da za ta kwantar da ransu.
Wa zai je ya ƙarfafa su
Domin su bauta wa Allah?
(AMSHI NA 3)
‘Ya Allah, aike ni! Zan je!
Zan koya musu Kalmarka.
Gata mafi girma ce Allah.
Ga ni, aike ni! Zan je!’
(Ka kuma duba Zab. 10:4; Ezek. 9:4.)