WAƘA TA 81
Rayuwar Majagaba
(Mai-Wa’azi 11:6)
-
1. Gari na wayewa kafin a yi rana,
Ko da muna jin barci
za mu fita yin wa’azi.
Muna yin fara’a ga mutanen yankin.
Muna dagewa ko
da suna saurara ko a’a.
(AMSHI)
Mu muka yi zaɓin,
Mu bayin Allah ne,
Duk abin da ya ce za mu yi.
Ko da me ya faru
Za mu yi wa’azi.
Ta hakan za mu nuna masa: “Ƙaunarmu.”
-
2. Sa’ad da mun dawo da faɗuwar rana,
Mun gaji, duk da haka
muna farin ciki sosai.
Muna ƙoƙartawa, muna son hidimar.
Mun gode wa Allah
domin yana mana albarka.
(AMSHI)
Mu muka yi zaɓin,
Mu bayin Allah ne,
Duk abin da ya ce za mu yi.
Ko da me ya faru
Za mu yi wa’azi.
Ta hakan za mu nuna masa: “Ƙaunarmu.”
(Ka kuma duba Josh. 24:15; Zab. 92:2; Rom. 14:8.)