Koma ka ga abin da ke ciki

Koma ga abubuwan da ke ciki

WAƘA TA 81

Rayuwar Majagaba

Rayuwar Majagaba

(Mai-Wa’azi 11:6)

  1. 1. Gari na wayewa kafin a yi rana,

    Ko da muna jin barci

    za mu fita yin wa’azi.

    Muna yin fara’a ga mutanen yankin.

    Muna dagewa ko

    da suna saurara ko a’a.

    (AMSHI)

    Mu muka yi zaɓin,

    Mu bayin Allah ne,

    Duk abin da ya ce za mu yi.

    Ko da me ya faru

    Za mu yi wa’azi.

    Ta hakan za mu nuna masa: “Ƙaunarmu.”

  2. 2. Sa’ad da mun dawo da faɗuwar rana,

    Mun gaji, duk da haka

    muna farin ciki sosai.

    Muna ƙoƙartawa, muna son hidimar.

    Mun gode wa Allah

    domin yana mana albarka.

    (AMSHI)

    Mu muka yi zaɓin,

    Mu bayin Allah ne,

    Duk abin da ya ce za mu yi.

    Ko da me ya faru

    Za mu yi wa’azi.

    Ta hakan za mu nuna masa: “Ƙaunarmu.”

(Ka kuma duba Josh. 24:15; Zab. 92:2; Rom. 14:8.)