WAƘA TA 83
Mu Yi Wa’azi “Gida-Gida”
(Ayyukan Manzanni 20:20)
-
1. Mu riƙa wa’azin Mulki
A dukan gidaje.
Mu nemi tumakin Allah
A dukan birane.
Ana shelar Mulkin Allah
A ko’ina yanzu.
Kamar yadda Yesu ya ce
Mu riƙa wa’azi!
-
2. Mu riƙa wa’azin Mulki,
Mu yi shi da ƙwazo.
Mu ba wa mutane dama
Su bauta wa Allah.
Suna bukatar taimako
Don su ɗaukaka shi.
Shi ya sa muke wa’azi
Don mu koyar da su.
-
3. Mu riƙa zuwa gidaje
Don mu yi wa’azi.
Amma su ne ke da zaɓin
Su saurari saƙon.
Wa’azinmu na ɗaukaka
Jehobah Allahnmu.
Mu nemi tumakin Allah
A dukan ƙasashe.
(Ka kuma duba A. M. 2:21; Rom. 10:14.)