WAƘA TA 87
Ku Zo Mu Sami Karfafa!
(Ibraniyawa 10:24, 25)
-
1. Muna cikin zamanin da ʼyan Adam
Suke cikin duhu sosai.
Bin umurnin Allah zai taimake mu
Don kada mu bijire fa.
Yin taro yana ƙarfafa ƙaunarmu
Da kuma bangaskiyarmu.
Yana sa mu yi ayyuka masu kyau,
Yana sa mu jimre sosai.
Ba za mu ƙi bin umurnin Allah ba,
Muna so mu yi nufinsa.
Yana koya mana nufin Jehobah,
Yana sa mu so gaskiya.
-
2. Jehobah Allah ya san bukatunmu,
Mu bi mizaninsa sosai.
Mugun ba zai iya rinjayar mu ba,
In muna halartan taro.
Muna koyan abubuwa da yawa
Daga ƙwararrun ’yan’uwa.
Dukan ’yan’uwanmu na taimakon mu,
Mun san ba mu kaɗaita ba.
Kuma kafin nufin Allah ya cika,
Mu riƙa halartan taro.
A taro, Jehobah na koya mana
Hikima da dokokinsa.
(Ka kuma duba Zab. 37:18; 140:1; Mis. 18:1; Afis. 5:16; Yaƙ. 3:17.)