Koma ka ga abin da ke ciki

Koma ga abubuwan da ke ciki

WAƘA TA 97

Kalmar Allah Za Ta Sa Mu Rayu

Kalmar Allah Za Ta Sa Mu Rayu

(Matta 4:4)

  1. 1. Kalmar Allah na ba da rai

    Mai inganci sosai.

    Kalmar tana da tamani,

    Fiye da abinci.

    Muna cin amfanin Kalmar,

    Yau da kuma gobe.

    (AMSHI)

    Wajibi ne mu karanta

    Kalmar Allah sosai.

    Karanta Kalmar za ta sa

    Mu amfana sosai.

  2. 2. Kalmar Allah na sa mu san

    Labaran mutane,

    Mutane amintattu fa,

    Masu gaba gaɗi.

    Karanta duk labarinsu

    Yana ƙarfafa mu.

    (AMSHI)

    Wajibi ne mu karanta

    Kalmar Allah sosai.

    Karanta Kalmar za ta sa

    Mu amfana sosai.

  3. 3. Koyaushe in mun karanta

    Kalmar Maɗaukaki,

    Tana ƙarfafa mu sosai,

    Tana sa mu jimre.

    In mun daraja Kalmarsa,

    Za mu sami bege.

    (AMSHI)

    Wajibi ne mu karanta

    Kalmar Allah sosai.

    Karanta Kalmar za ta sa

    Mu amfana sosai.

(Ka kuma duba Josh. 1:8; Rom. 15:4.)