WAƘA TA 100
Mu Rika Marabtar Baki
(Ayyukan Manzanni 17:7)
-
1. Jehobah na mana alheri sosai,
Yana kula da dukan halittunsa.
Yana yin tanadi,
ga dukan ’yan Adam
Domin su ji daɗin rayuwa.
In muna taimaka wa duk mutane,
Muna yin koyi da Jehobah Allah.
Jehobah Allah zai
yi mana albarka
Don muna yin alheri sosai.
-
2. In muna taimaka wa mabukata,
Jehobah zai saka mana fa sosai.
Ko da su baƙi ne,
mu taimaka musu,
Su iya biyan bukatunsu.
Lidiya ta marabci baƙi sosai,
Mu ma mu yi koyi da misalinta.
Allah ba zai manta
da waɗanda suke
Yin koyi da alherinsa ba.
(Ka kuma duba A. M. 16:14, 15; Rom. 12:13; 1 Tim. 3:2; Ibran. 13:2; 1 Bit. 4:9.)