WAƘA TA 105
“Allah Kauna Ne”
(1 Yohanna 4:7, 8)
-
1. Allahnmu mai ƙauna ya ce:
‘Ku zo ku bi hanyata.’
Za mu nuna wa Jehobah
Da maƙwabtanmu ƙauna.
Hakan rayuwa mai kyau ce,
Rayuwar da muke so.
Ƙaunar Kristi ba iyaka,
Za mu riƙa nuna ta.
-
2. Ƙaunarmu ga Maɗaukaki
Tana sa mu yi ƙauna.
Allahnmu zai taimake mu
In mun daina bin hanya.
Ƙauna ba ta yin ƙiyayya,
Tana jimre da kome.
Mu riƙa ƙaunar ’yan’uwa,
Mu ji daɗin ƙaunar nan.
-
3. Kar mu riƙa yin ƙiyayya,
Kar ta yi kusa da mu.
Jehobah Allah mai ƙauna
Ya koyar da mu cewa:
Mu so Shi da maƙwabtanmu,
Mu nuna ƙauna sosai.
Mu riƙa nuna wa kowa
Ƙauna daga zuciya.
(Ka kuma duba Mar. 12:30, 31; 1 Kor. 12:31–13:8; 1 Yoh. 3:23.)