WAƘA TA 125
Masu Jinkai Suna Farin Ciki!
(Matta 5:7)
-
1. Jehobah na da tausayi
Kuma yana son mu sosai.
Shi mai son yin nagarta ne,
Yana biyan bukatunmu.
In muka yi kurakurai
Kuma muka yi addu’a.
Jehobah zai gafarce mu
Don ya san ajizai ne mu.
-
2. In muka yi tuban gaske
In muna son gafartawa,
Yesu Kristi ya ce mana
In mun yi addu’a mu ce:
‘Allah ka gafarta mana,
Yadda muke gafartawa.’
In mun yafe wa mutane,
Za mu sami kwanciyar rai.
-
3. In muna son ba da kyauta,
Muna yin koyi da Allah.
Mu taimaki mabukata,
Mu yi hakan da yardar rai.
Jehobah Allah mai ƙauna,
Zai albarkace mu sosai.
Masu jinƙai suna murna,
Allah yana daraja su.
(Ka kuma duba Mat. 6:2-4, 12-14.)