WAƘA TA 133
Mu Bauta wa Jehobah da Kuruciyarmu
(Mai-Wa’azi 12:1)
-
1. Allah yana ƙaunar mu matasa,
Mu bauta masa da duk ƙarfinmu.
Don haka, zai riƙa kula da mu,
Zai albarkace mu har abada.
-
2. Mu riƙa daraja iyayenmu
Domin suna kula da mu sosai.
Allah da mutane za su so mu,
Kuma za mu kusaci Jehobah.
-
3. Mu riƙa tunawa da Jehobah,
Mu ci gaba da son koyarwarsa.
Mu riƙa yin iya ƙoƙarinmu, don hakan
Zai sa Jehobah murna.
(Ka kuma duba Zab. 71:17; Mak. 3:27; Afis. 6:1-3.)