Koma ka ga abin da ke ciki

Koma ga abubuwan da ke ciki

WAƘA TA 145

Allah Ya Yi Mana Alkawarin Aljanna

Allah Ya Yi Mana Alkawarin Aljanna

(Ru’ya ta Yohanna 21:4)

  1. 1. Allah zai dawo da aljanna

    Ta sarautar Yesu Kristi.

    Zai kawar da dukan zunubi

    Da mutuwa da azaba.

    (AMSHI)

    Yin rayuwa a Aljanna,

    A duniya zai yi daɗi.

    Allah zai sa Ɗansa Yesu,

    Ya cika alkawuran nan.

  2. 2. A aljanna Jehobah zai sa

    Ɗansa ya ta da matattu.

    Yesu ya ce: ‘Za ka kasance

    Tare da ni a Aljanna.’

    (AMSHI)

    Yin rayuwa a Aljanna,

    A duniya zai yi daɗi.

    Allah zai sa Ɗansa Yesu,

    Ya cika alkawuran nan.

  3. 3. Yesu Kristi ne Sarkin Mulkin,

    Shi ne Sarkin da ya dace.

    Muna murna don albarkun nan,

    Muna yabon Jehobah fa.

    (AMSHI)

    Yin rayuwa a Aljanna,

    A duniya zai yi daɗi.

    Allah zai sa Ɗansa Yesu,

    Ya cika alkawuran nan.

(Ka kuma duba Mat. 5:5; 6:10; Yoh. 5:​28, 29.)