WAƘA TA 145
Allah Ya Yi Mana Alkawarin Aljanna
(Ru’ya ta Yohanna 21:4)
-
1. Allah zai dawo da aljanna
Ta sarautar Yesu Kristi.
Zai kawar da dukan zunubi
Da mutuwa da azaba.
(AMSHI)
Yin rayuwa a Aljanna,
A duniya zai yi daɗi.
Allah zai sa Ɗansa Yesu,
Ya cika alkawuran nan.
-
2. A aljanna Jehobah zai sa
Ɗansa ya ta da matattu.
Yesu ya ce: ‘Za ka kasance
Tare da ni a Aljanna.’
(AMSHI)
Yin rayuwa a Aljanna,
A duniya zai yi daɗi.
Allah zai sa Ɗansa Yesu,
Ya cika alkawuran nan.
-
3. Yesu Kristi ne Sarkin Mulkin,
Shi ne Sarkin da ya dace.
Muna murna don albarkun nan,
Muna yabon Jehobah fa.
(AMSHI)
Yin rayuwa a Aljanna,
A duniya zai yi daɗi.
Allah zai sa Ɗansa Yesu,
Ya cika alkawuran nan.
(Ka kuma duba Mat. 5:5; 6:10; Yoh. 5:28, 29.)