WAƘA TA 148
Jehobah Zai Cece Bayinsa
(2 Sama’ila 22:1-8)
-
1. Jehobah ayyukanka sun nuna mini,
Kai ne Mahaliccin
sammai da duniya.
Na san ka kusan cire duk masu yin
—mugunta
A duniyar nan fa.
(AMSHI)
Jehobah zai taimaki mai aminci.
Allahnmu zai ceci dukan aminansa.
Mu dogara da ikon Allah
da cetonsa,
Mu yabe shi, mu yi wa’azin
bisharar nan.
-
2. Maƙiyana suna so su hallaka ni.
“Jehobah Allahna,
na dogara da kai.”
Ka ji kukana da addu’o’ina,
“Allahna
Ka kāre ni sosai.”
(AMSHI)
Jehobah zai taimaki mai aminci.
Allahnmu zai ceci dukan aminansa.
Mu dogara da ikon Allah
da cetonsa,
Mu yabe shi, mu yi wa’azin
bisharar nan.
-
3. Jehobah zai hallaka
duk maƙiyansa.
Dukan amintattu
za su rera yabo.
Duk abin da kake so za ka zama,
Ubanmu,
Za mu sami ceto.
(AMSHI)
Jehobah zai taimaki mai aminci.
Allahnmu zai ceci dukan aminansa.
Mu dogara da ikon Allah
da cetonsa,
Mu yabe shi, mu yi wa’azin
bisharar nan.
(Ka kuma duba Zab. 18:1, 2; 144:1, 2.)