Koma ka ga abin da ke ciki

14 GA YULI, 2016
RASHA

Kotu Za Ta Saurari Karar da Shaidun Jehobah Suka Daukaka Game da Barazanar Rufe Ofishinsu da Ke Rasha

Kotu Za Ta Saurari Karar da Shaidun Jehobah Suka Daukaka Game da Barazanar Rufe Ofishinsu da Ke Rasha

Kotun Gunduma ta Tver da ke Moscow ta amince ta saurari karar da Shaidun Jehobah suka daukaka game da barazanar da Mai Shigar da Kara a Madadin Gwamnati ya yi na kokarin rufe ofishinsu da ke kasar. Kotun za ta saurari karar a ranar 18 ga Yuli, 2016 don ta ga ko barazanar tana bisa ka’ida.

’Yan majalisa da ke birnin Arkhangelsk su ma sun kai karar Shaidun Jehobah a wurin Ministan Shari’a mai suna Aleksandr Konovalov. A karar da suka shigar, sun bukaci gwamnati ta kafa doka da za ta sa a rufe ofishin Shaidun Jehobah da kuma hana su gudanar da ayyukansu na ibada a kasar gaba daya.