1 KORINTIYAWA 7-9
DARUSSA DAGA KALMAR ALLAH |Albarkar Kasancewa Marasa Aure
7:32, 35, 38
Tun da daɗewa, Kiristoci da yawa sun gano cewa kasancewa marar aure yana kawo albarka sosai. Yana ba su damar ƙara ƙwazo a hidimarsu da yin tarayya da mutane dabam-dabam da kuma sa su kusaci Jehobah sosai.
DON BIMBINI: Idan ba ka da aure, me za ka yi don ka ji daɗin bauta wa Allah?
Mene ne ’yan’uwa a ikilisiya za su yi don su ƙarfafa da kuma taimaka wa waɗanda ba su yi aure ba?