1 KORINTIYAWA 14-16
DARUSSA DAGA KALMAR ALLAH |Allah Zai Zama “Kome da Kome” ga Kowa
15:24-28
Waɗanda suka riƙe amincinsu ga Jehobah har ƙarshe za su sami albarka sosai a nan gaba. Idan muna gaya wa mutane game da alkawuran da ya yi mana da fara’a, hakan yana sa mu ƙara gaskata da alkawuransa. Manzo Bulus ya ƙarfafa Kiristoci cewa su riƙa tunanin lokacin da Yesu Kristi zai gama sarautarsa na shekara dubu kuma Jehobah ya zama “kome da kome” ga kowa.
Waɗanne albarka ne ka fi so kuma me ya sa?
Me ya tabbatar maka da cewa Allah zai cika alkawuransa?