Koma ka ga abin da ke ciki

Koma ga abubuwan da ke ciki

RAYUWAR KIRISTA

Kasar Ta “Shanye Ruwan Kogin”

Kasar Ta “Shanye Ruwan Kogin”

A zamanin dā, hukumomin gwamnati sun taimaka wa bayin Jehobah. (Ezr 6:​1-12; Es 8:​10-13) Ko a yanzu ma, muna ganin yadda “ƙasar,” wato wasu hukumomi da suke da kirki a zamanin nan suke shanye “ruwan kogin” ko kuma dakatar da tsanantawa da “dodon” nan wato Shaiɗan yake sa a yi wa mutanen Allah. (R. Yar 12:16) A wasu lokuta, Jehobah, “Allah na ceto” yakan sa hukumomi su taimaka wa mutanensa.​—Za 68:20; K. Ma 21:1.

Me za ka yi idan aka saka ka a fursuna don imaninka? Ka tabbata cewa Jehobah yana gani kuma zai kula da kai. (Fa 39:​21-23; Za 105:​17-20) Ban da haka ma, Jehobah zai albarkace ka don bangaskiyarka kuma amincinka zai ƙarfafa ’yan’uwa a faɗin duniya.​—Fib 1:​12-14; R. Yar 2:10.

KU KALLI BIDIYON NAN AN SAKI ’YAN’UWA DAGA GIDAN YARI A KORIYA, SAI KU AMSA TAMBAYOYI NA GABA:

  • Me ya sa an yi shekaru ana saka ’yan’uwanmu da yawa a fursuna a Koriya ta Kudu?

  • Wane mataki ne hukumomi suka ɗauka da ya sa aka sako ’yan’uwanmu tun lokacinsu bai yi ba?

  • Ta yaya za mu taimaka wa ’yan’uwanmu da suke fursuna domin imaninsu a faɗin duniya?

  • Ta yaya za mu yi amfani da ’yancin da muke da shi yanzu?

  • Waye yake taimaka mana mu yi nasara a shari’a da yawa da muke yi?

Ta yaya nake amfani da ’yancin da nake da shi?