RU’UYAR DA AKA YI WA YOHANNA 4-6
DARUSSA DAGA KALMAR ALLAH |Fitowar Mahaya Hudu
6:2, 4-6, 8
Yesu “ya ƙara cin nasara” ta wajen yin yaƙi da Shaiɗan da aljanunsa a sama kuma ya jefo su nan duniya. Ba za su iya sake komawa sama ba. Yesu ya ci gaba da yin nasara a madadin bayinsa ta wajen taimaka musu da kuma kāre su a wannan kwanakin ƙarshe. Zai gama “cin nasara” sa’ad da ya halaka sauran mahaya ukun a yaƙin Armageddon. Bayan haka, zai mai da duniyar nan aljanna.